Sojojin Isra'ila Sun Kai Farmaki A Yankin Zirin Gaza
Sojojin Haramtacciyar kasar Isra'ila sun kai hare-hare kan wuraren kungiyar gwagwarmayar Palastinawa a gabashin sansanin Albarij na Zirin Gaza a wannan Talata
Cibiyar yada labaran Palastinu ta habarta cewa dakarun tsaron Isra'ila sun kai farmaki har ila yau a yankuna da dama na kusa na sansanin Al-Auda na gabashin Albarij. inda suka yi da'awar cewa sun kai harin ne a yayin da wasu matasan Palastinawa suke yin yunkurin shiga cikin haramtacciyar kasar Isra'ila.
Har ila yau a jijjifin safiyar yau Talata, sojojin Isra'ilan sun kai hari a buranan Qudus, Alkhalil da Ramulla dake gabar tekun Jodan tare kuma da yin awan gaba da wasu matasan Palastinawa 11.
A ko wata rana Sojojin Isra'ila na kai farmaki gidajen Palastinawa a yankin gabar tekun Jodan da Qudus, alkaluma sun nuna cewa akwai palastinawa 6500 cikinsu hardakananen yara kimanin 300 a gidajen yarin Isra'ila.