Sabon Fira Ministan Guinea Conakry Ya Sanar Da Sunayen Sabbin Ministocinsa
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i31194-sabon_fira_ministan_guinea_conakry_ya_sanar_da_sunayen_sabbin_ministocinsa
Sabon fira ministan kasar Guinea Conakry ya sanar da sunayen sabbin ministocinsa tare da barin wasu tsoffin ministocin a kan mukamansu.
(last modified 2018-08-22T07:01:53+00:00 )
May 28, 2018 02:22 UTC
  • Sabon Fira Ministan Guinea Conakry Ya Sanar Da Sunayen Sabbin Ministocinsa

Sabon fira ministan kasar Guinea Conakry ya sanar da sunayen sabbin ministocinsa tare da barin wasu tsoffin ministocin a kan mukamansu.

Kamfanin dillancin labaran Faransa ya watsa rahoton cewa: A wata sanarwa da sabon fira ministan kasar Guinea Conakry ya fitar a cikin daren Asabar: Ibrahim Kassory Fofana ya bayyana sunayen mutane 33 a matsayin sabbin ministocinsa duk da cewa tsoffin ministocin tsaro, harkokin waje, shari'a da na harkokin gudanar da jihohi ya bar su a kan mukamansu na baya.

A ranar Litinin 21 ga wannan wata na Mayu ne shugaban kasar Guinea Conakry Alpha Conde ya sanar da Ibrahim Kassory Fofana a matsayin sabon fira ministan kasar a kokarin da yake yi na ganin ya shawo kan rikicin siyasar da ya kunno kai a kasar sakamakon zargin da 'yan adawar kasar ke yi cewa yana son yin tazarce a zaben shekara ta 2020.

Kafin nadin nasa a matsayin sabon fira ministan Guinea Ibrahim Fofana shi ne ministan ma'aikatar zuba hannun jari ta kasar a tsohuwar gwamnatin fira minista Mamady Youla da ta yi murabus a makon da ya gabata..