Sojojin Yemen Sun Harba Makamai Masu Linzami Akan Babban Birnin Saudiyya
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i32020-sojojin_yemen_sun_harba_makamai_masu_linzami_akan_babban_birnin_saudiyya
A daren jiya ne sojojin kasar ta Yemen su ka kai wa birnin Riyadh hari
(last modified 2018-08-22T07:02:01+00:00 )
Jun 25, 2018 03:39 UTC
  • Sojojin Yemen Sun Harba Makamai Masu Linzami Akan Babban Birnin Saudiyya

A daren jiya ne sojojin kasar ta Yemen su ka kai wa birnin Riyadh hari

Kamfanin dillancin labarun reuters ya ce; An ji karar fashewar wasu abubuwa masu karfi da kuma ganin hasken wuta a saman birnin Riyadh.

A can kasar Yemen sojojin kasar sun sanar da harba makamai masu linzami  samfurin "Burkan H 2" akan ma'aikatar tsaron Saudiyya da kuma wasu cibiyoyin gwamnatin kasar a cikin birnin Riyadh.

Kakakin sojan Yeman Sharaf Lukman ya jaddada cewa; Za su ci gaba da kai hare-hare da makamai masu linzami akan cibiyoyin tattalin arziki na Saudiyya matukar Saudiyyar ba ta daina kai wa kasar Yemen hari ba.

Tun a cikin watan Maris na 2015 ne dai Saudiyyar take jagorantar kawancen yaki da kasar Yemen, wanda kawo ya zuwa yanzu ya ci rayukan mutane fiye da 12.000.