Syria: Wani Kwamandan "Yan Ta'adda Ya Mika Kai Ga Sojojin Gwamnati
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i32269-syria_wani_kwamandan_yan_ta'adda_ya_mika_kai_ga_sojojin_gwamnati
Majiyar tsaron kasar Syria ta ce wani daga cikin kwamandojin kungiyar Syrian Free Army mai suna Adham al-Akrad, ya mika kansa ga sojojin kasar a yankin Dar'aa.
(last modified 2018-08-22T07:02:05+00:00 )
Jul 10, 2018 08:03 UTC
  • Syria: Wani Kwamandan

Majiyar tsaron kasar Syria ta ce wani daga cikin kwamandojin kungiyar Syrian Free Army mai suna Adham al-Akrad, ya mika kansa ga sojojin kasar a yankin Dar'aa.

Majiyar ta ci gaba da cewa Adham al-Akrad ya kuma mika makaman da suke a karkashinsa da rundunarsa.

A gefe daya kungiyar kare hakkin dan adam ta : "Human Right Watch" ta ambato majiyar 'yan ta'adda ta babbatar da cewa sojojin kasar ta Syria sun shimfida ikonsu a yankuna masu fadi na Dar'aa. A cikin kwanaki 18 da suka gabata ne sojojin Syria suka kashe 'yan ta'adda 131 a cikin yankin na Dar'aa.

A karshen watan Yuni ne dai sojojin na Syria suka bude kai farmaki akan tungar 'yan ta'addar kungiyar; Syrian Free Army' a yankin Dar'aa da ke kan iyaka da kasar Jordan. Kawo ya zuwa yanzu kaso 90% na gundumar Dar'aa ta koma karkashin ikon gwamnatin Syria, bayan da aka fatattaki 'yan ta'adda daga ciki.