Yemen: Zanga-zangar Nuna Kin Amincewa Da Mamayar Saudiyya
Mazauna garin al-Muhrah da ke gabacin kasar Yemen sun yi Zanga-zangar yin kira ga sojojin Saudiyya da su fice daga kasar
Da marecen jiya juma'a ne mazauna garin na Muhrah su ka gudanar da Zanga-zangar suna masu yin tir da duk wani yunkuri na raunana hurumi da 'yancin kasar Yemen da cin gashin kanta
A gefe daya jiragen yakin Saudiyya da na Hadaddiyar Daular Larabawa suna ci gaba da kai hare-hare a yankuna daban-daban na kasar da su ka hada da al-Hudaidah.
A shekarar da ta gabata ne dai sojojin na Saudiyya da na Hadaddiyar Daular Larabawa su ka bude sansani a yankin na al-Muhrah da sunan fada da fasa kwauri.
Yakin da Saudiyya ta shelanta a cikin kasar Yemen a 2015 ya shiga cikin shekara ta 4 ba tare da ta cimma wata manufa ba.