Saudiyya Na Ci Gaba Da Kai Hari A Garin Hudaidah
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i34009-saudiyya_na_ci_gaba_da_kai_hari_a_garin_hudaidah
Harin da Jiragen Yakin Saudiyyar su ka kai a yankin 7 ga watan Yuni, karamin yaro daya ya rasa ransa, yayin da wasu mutane 7 suka jikkata
(last modified 2018-11-09T15:36:27+00:00 )
Nov 09, 2018 15:36 UTC
  • Saudiyya Na Ci Gaba Da Kai Hari A Garin Hudaidah

Harin da Jiragen Yakin Saudiyyar su ka kai a yankin 7 ga watan Yuni, karamin yaro daya ya rasa ransa, yayin da wasu mutane 7 suka jikkata

Tashar talabijin din al-masirah ta ba da labarin cewa; A sanadiyyar harin na Saudiyya gidajen fararen hula da dama sun rushe tare da haddasa asara ga dukiyoyinsu.

A jiya alhamis ma dai sojojin na Saudiyya sun kai wasu hare-haren har sau 30 a yankin da kae kira Kilo 60 da kuma babban titin Sittin da suke a cikin birnin na Hudaidah.

Garin al-Hudaidah yana da matukar muhimmanci saboda tashar jirgin ruwan da take cikinsa wacce ake shigar da kayan abinci cikin kasar da kaso 70%

Harin da Saudiyyar take kai wa a birnin Hudaidah yana samun cikakken goyon bayan sojojin Amurka da na Birtaniya kamar yadda kafafen watsa labarun Amurka suka ambata.

A cikin shekaru uku na yakin da Saudiyya ta shelanta akan Yemen fiye da mutane 13,000 su ka kwanta dama, yayin da wasu dubbai su ka jikkata.

Bugu da kari, hare-haren na Saudiyya sun yi sanadiyyar lalata asibitoci da cibiyoyin shan magani kamar kuma yadda su ka jefa kasar cikin yunwa saboda rashin abinci.