Mutum 30 Sun Mutu A Ruftawar Mahakar Zinari A Afganistan
Jan 06, 2019 07:52 UTC
Rahotanni daga Afganistan na cewa mutum akalla 30 ne suka rasa rayukansu biyo bayan ruftawar wata mahakar zinari a arewa maso gabashin kasar.
Da yake tabbatar da hakan ga amfanin dilancin labaren AFP gwamnan yankin Mohammad Rustam Raghi ya ce akwai kuma wasu mutane bakwai da suka samu raunuka a lamarin.
Lamarin dai ya auke ne a lardin Kohistan, na jihar Badakhshan.