Afganistan : Bam Ya Kashe Mutane 28 A Kabul
Apr 19, 2016 05:03 UTC
Rahotanni daga Afganistan na cewa akalla mutane 28 ne suka rasa rayukan su a harin da kungiyar Taliban ta dauki alhakin kaiwa a birnin Kaboul.
Harin da aka kai da wata mota a wannan safiyar yayi kuma jikkata mutune sama da 200.
Wasu rahotanni na daban sun ce an yi ta harbe-harbe daga bisanin harin, lamarin da yayi sanadin mutuwar fararen hula da dama da kuma jami'an tsaro.
An dai kai hari ne a harabar ma'aikatar tsaron kasar dake Kaboul.
Tuni dai shugaban kasar Ashraf Ghani ya fitar da sanarwar yin allawadai da wannan harin.