Harin ta'addanci ne ya kado jirgin fasinjan kasar Masar
May 24, 2016 07:58 UTC
Wata kotu a Masar ta ce jirgin fasinjan kasar da ya fado an kai masa harin ta'addanci ne.
Kamfanin dillancin labarun Associated Press ya ambato wata majiyar shari'ar kasar masar na cewa; Bisa la'akari da sassan jikin wasu matafiya da aka samu, da akwai yiyuwar an kai harin ta'addanci ne.
Majiyar Kotun kasar ta Masar din ta kuma ce; jirgin saman ya tarwaste ne kuma ya fadi a cikin sassa daban-daban na ruwan Metrenia. Hakan, in ji kotun yana nuni ne da yadda jirgin ya tarwatse a sama tun kafin ya fada kan ruwa.
Mutane 66 ne dai su ka rasa raukansu a hatsarin.