Harin Ta'addanci A Kasar Yamen
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i7699-harin_ta'addanci_a_kasar_yamen
Mota Makare da Bama-Bamai da ta tashi a Birnin Aden ta kashe mutane da dama.
(last modified 2018-08-22T06:58:33+00:00 )
Jul 06, 2016 01:47 UTC
  • Harin Ta'addanci A Kasar Yamen

Mota Makare da Bama-Bamai da ta tashi a Birnin Aden ta kashe mutane da dama.

Majiyar Kamfanin Dillancin Labarun ( AFP) ta ce; An kai wa filin saukar jiragen sama na Aden hari da motoci biyu masu makare da bama-bamai, da hakan yayi sanadin mutuwar mutane 6.

Majiyar filin saukar jiragen saman na Aden ta ce; Motar farko ta tarwatsa kofar shiga cikin filin sauka jiragen, saboda haka mota ta biyu ta sami damar shiga cicki.

A gefe daya, fada ya barke a tsakanin sojojin kasar da kuma maharan a cikin wani sansani da ke killace.

Kungiyar alqa'eda a tsibirin larabawa dai ta kara fadada hare-harenta a cikin Yeman, tun bayan da saudiyya ta shelanta akan wannan kasa.

Kawo ya zuwa yanzu dai dubban mutane su ke kwanta dama a kasar ta Yamen.