Mutanen Birnin Sirt Na Kasar Libya Sun Fara Komawa Gidajensu
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i8869-mutanen_birnin_sirt_na_kasar_libya_sun_fara_komawa_gidajensu
Mutanen birnin Sirt a kasar Libya sun fara komawa gidajensu.
(last modified 2018-08-22T06:58:40+00:00 )
Jul 29, 2016 23:18 UTC
  • Mutanen Birnin Sirt Na Kasar Libya Sun Fara Komawa Gidajensu

Mutanen birnin Sirt a kasar Libya sun fara komawa gidajensu.

A dai dai lokacinda sojojin kasar Libya suke kara samun galaba a kan mayakan kungiyar Daesh a birnin Sirt na kasar Libya mutanen birnin sun fara dawowa gidajensu. Tashar Television ta Euronews ta bayyana cewa a lokacinda maykan kungiyar Daesh ta kwace iko da birnin a cikin watan Yuni shekara 2015 kimanin kashi 3/4 na mutanen garin sun bar gidajensu. 

A halin yanzu dai sojojin kasar ta Libya tare da taimakon sojojin majalisar dinkin duniya suna ci gaba da samun galaba a kan mayakan na Daesh.  Har'ila yau sojojin kasar ta Libya suna binciken gida gida don tabbatar da dukkan mayakan Desh sun fice daga binin. A cikin watan Yuli na wannan shekara na sojojin kasar ta Libya suka far yiwa mayakan Daesh kofar rako a biniam na Sirt. Tun cin shekara ta 2011 mayakan Daesh suka fara share wuri don mamayar birnin na bkin nruwa.