-
Fira Ministan Burkina Faso Ya Yi Murabus
Jan 19, 2019 14:07Fira ministan Burkina Faso, Paul Kaba Thieba, ya yi murabus tare da sauren manbobin gwamnatinsa.
-
Gabon : Bongo, Ya Koma Morocco Don Ci Gaba Da Jinya
Jan 17, 2019 05:04Shugaba Ali Bongo Odimba na Gabon, ya koma jinya a kasar Morocco, kasa da sa'o'i 24 bayan ya koma koma gida inda ya halarci bikin rantsar da sabuwar gwamnati.
-
Kotun ICC, Ta Yi Watsi Da Sallamar Laurent Gbagbo
Jan 17, 2019 04:06Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, ICC, ta dakatar da sakin tsohon shugaban kasar Ivory Coast, Laurent Gbagbo, bayan da masu shigar da kara na kotun suka daukaka kara.
-
ICC Za Ta Daukaka Kara Kan Sallamar Laurent Gbagbo
Jan 16, 2019 10:27Masu shigar da kara na kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, ICC, zasu daukaka kara ga umurnin da wasu lauyoyin kotun suka bayar na sallamar tsohon shugaban kasar Ivory Coast, Laurent Gbagbo, wanda ake zargi da cin zarafin bil adama.
-
Kenya : Harin Al'shebab Ya Kashe Mutum 5 A Nairobi
Jan 15, 2019 16:42Kungiyar Al-shebab ta dauki alhakin kai wani hari data ce mayakan ta ne suka kai shi a Nairobi babban birnin kasar.
-
Gabon : Ali Bongo Ya Koma Libreville
Jan 15, 2019 16:15Shugaba Ali Bongo Odimba na Gabon, ya koma kasarsa a cikin daren jiya Litini, bayan shafe sama da wata biyu na jinya a kasashen waje.
-
Zimbabwe : An Kashe Mutum Uku A Zanga zanga
Jan 15, 2019 15:42Rahotanni daga Zimbabwe na cewa mutum uku ne aka kashe a zanga zangar data barke a kasar tun jiya Litini, biyo bayan matakin gwamnati na linka farashin man fetur a wannan kasa dake fama da matsalar tattalin arziki.
-
Kotun ICC Ta Sallami Tsohon Shugaban Ivory Coast
Jan 15, 2019 15:24Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta sallami tsohon shugaban kasar Ivory Coast Laurent Gbagbo, da kuma tsohon ministansa Charles Ble Goude da take tsare da buisa zargin cin zarafin bil adama.
-
Rashin Tsaro : Buhari Na Najeriya Ya Sake Zargin Gaddafi
Jan 14, 2019 04:56Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya, ya sake zargin tsohon shugaban kasar Libiya, mirigayi Muammar Ghaddafi da zame ummul-aba'isin tabarbarewar al'amuran tsaro a kasashen yammacin Afrika dana tsakiya da dama.
-
Kungiyar (SADC), Ta Bukaci A Sake Kidayar Kuri'un Zabe A D.R Congo
Jan 14, 2019 03:34Kungiyar ci-gaban kasashen kudancin Afirka (SADC), ta bada shawarar a sake kidayar kuri'un zabe a Jamhuriya Demokuradiyyar Congo, domin kwantar da hankali a takaddamar data kunno kai bayan sanar da sakamakon wucin gadi na zaben shugaban kasar.