Gabon : Bongo, Ya Koma Morocco Don Ci Gaba Da Jinya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34837-gabon_bongo_ya_koma_morocco_don_ci_gaba_da_jinya
Shugaba Ali Bongo Odimba na Gabon, ya koma jinya a kasar Morocco, kasa da sa'o'i 24 bayan ya koma koma gida inda ya halarci bikin rantsar da sabuwar gwamnati.
(last modified 2019-01-17T05:04:10+00:00 )
Jan 17, 2019 05:04 UTC
  • Gabon : Bongo, Ya Koma Morocco Don Ci Gaba Da Jinya

Shugaba Ali Bongo Odimba na Gabon, ya koma jinya a kasar Morocco, kasa da sa'o'i 24 bayan ya koma koma gida inda ya halarci bikin rantsar da sabuwar gwamnati.

Shugaba Bongo, wanda ya kamu da rashin lafiya a ranar 24 ga watan Oktoba na 2018 data gabata a Saudiyya, ko koma a birnin Rabah na kasar Morocco inda yake ci gaba da karbar magani.

A safiyar ranar Talata, shugaba Bongo, ya halarci bikin rantsar da sabuwar gwamnatins amai ministoci 38 a fadar shugaban kasar dake Libreville, saidai bikin ba'a gayyaci jama'a da 'yan jarida a bikin ba.

'Yan kasar dai sun samu ganinshi a wani faifan bidiyo da kafofin yada labarai na kasar suka wallafa.

Komawarsa gida na zuwa ne kwanaki kadan bayan yunkurin yujin mulkin da akayi wa gwamnatinsa,.wanda baiyi nasara ba.