Mar 07, 2019 04:47
Hukumar zabe mai zaman kanta a kasar Tunisia ta sanar da ranar 6 ga watan Oktoba mai zuwa a matsayin ranar da za'a gudanar da zaben 'yan majalisar dokokin kasar, a yayin da za'a gudanar da zaben shugaban kasa kuma a ranar 10 ga watan Nuwamba a cikin wannan shekara.