-
Kotun Kolin Gabon Ta Ki Amincewa Da Shigowar Masu Sanyan Idon AU Wajen Sake Kidayar Kuri'u
Sep 21, 2016 12:04Kotun koli ta kasar Gabon ta sanar da cewa babu bukatar masu sanya idon na kungiyar Tarayyar Afirka su shigo kasar don sanya ido kan sake hukuncin da za ta fitar dangane da batun sakamakon zaben shugaban kasar da aka gudanar wanda ya haifar da rikici na siyasa a kasar.
-
AU Za Ta Aika Da Masu Sa Ido Kan Shariar Daukaka Kara kan Zaben Gabon
Sep 15, 2016 05:54Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta sanar da cewa tana shirin aikewa da masu sanya ido don taimakawa Kotun Kundin Tsarin Mulki na kasar Gabon wajen dubi cikin kukan da shugaban 'yan adawar kasar Jean Ping ya shigar yana zargin shugaba Ali Bongo na kasar da magudi a zaben shugaban kasar da aka gudanar a watan da ya gabata.
-
Sabuwar Gwamnatin Kasar Zambiya Ta Kama Aiki, Bayan Rantsar Da Shugaba Lungu
Sep 13, 2016 18:48A yau ne zababben shugaban kasar Zambiya Edgar Lungu ya yi rantsuwar kama aiki a wani sabon wa'adi na shugabancin kasar lamarin da ke nufin daga yau sabuwar gwamnatin kasar ta fara aikinta kenan duk kuwa da korafe korafen da 'yan adawa suke yi.
-
Mutane Gabon Na Ci Gaba Da Nuna Rashin Amincewa Da Rikicin Siyasa A Kasar
Sep 11, 2016 05:56Rahotanni daga kasar Gabon sun bayyana cewar daruruwan mutanen kasar sun gudanar da wata zanga-zanga don nuna rashin amincewarsu da ci gaba da rikicin siyasa da ke faruwa a kasar bayan sanar da sakamakon shugaban kasar da aka yi.
-
Babban Kotun Zambiya Ta Ki Amincewa Da Hana Rantsar Da Shugaban Kasar
Sep 11, 2016 05:55Babbar kotun kasar Zambiya ta yi watsi da bukatar da babbar jam'iyyar adawa da ta kasar UPND ta gabatar na a hana rantsar da shugaban kasar Edgar Lungu a wa'adin mulki na gaba da ake sa ran yi a jibi Talata, saboda zargin cewa an tafka magudi a zaben shugaban kasar da aka gudanar.
-
Tarayyar Afirka Za Ta Shiga Tsakani Don Magance Rikcin Zaben Kasar Gabon
Sep 07, 2016 05:57Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta sanar da cewa aniyarta na turawa da wata tawaga ta manyan jami'anta zuwa kasar Gabon don shiga tsakani da nufin kawo karshen rikicin siyasa da ya bullo kai a kasar bayan sanar da sakamakon zaben shugaban kasar da aka gudanar inda aka sanar da shugaban kasar Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben.
-
Jagoran 'Yan Adawan Gabon Yayi Kiran Da Gudanar Da Yajin Aiki Na Gama Gari
Sep 05, 2016 16:11Jagoran 'yan adawan kasar Gabon wanda kuma aka sanar da ya kashe kaye a zaben shugaban kasar da aka gudanar Jean Ping ya yi kiran da a fara yajin aiki na gama gari a duk fadin kasar don nuna rashin amincewa da sakamakon zaben da aka sanar inda aka ce shugaban kasar Ali Bongo ne ya lashe zaben.
-
Ana Shirin Rantsar Da Shugaban Zambiya Bayan Watsi Da Karar Abokin Hamayya
Sep 05, 2016 16:11Kotun kundin tsarin mulkin kasar Zambiya ta yi watsi da karar da dan takarar da ya sha kaye a zaben shugaban kasar da aka gudanar Hakainde Hichilema lamarin da zai share fagen rantsar da shugaban kasar Edgar Lungu a wani wa'adi na shekaru biyar a kan karagar mulkin kasar
-
Mutane Uku Sun Mutu A Rikicin Bayan Zaben Shugaban Kasar Gabon
Sep 01, 2016 17:21Rahotanni daga kasar Gabon sun bayyan cewar alal akalla mutane 3 sun rasa rayukansu kana wasu daruruwa kuma suna hannu 'yan sanda biyo bayan rikicin da ya barke a kasar bayan sanarwar da aka yi cewa shugaban kasar mai ci Ali Bongo shi ne ya lashe zaben shugaban kasar da aka gudanar a ranar Asabar din da ta gabata.
-
Kungiyar EU Ta Yi Zargin Tafka Magudi A Zaben Shugaban Kasar Gabon
Aug 30, 2016 05:55A daidai lokacin da ake jiran fitar da sakamakon zaben shugaban kasar da aka gudanar a kasar Gabon a hukumance, masu sa ido daga kungiyar Tarayyar Turai sun bayyana cewar akwai yiyuwar an tafka magudi a zaben shugaban kasar.