Malaysia Ta Kori Jakadan Koriya Ta Arewa
https://parstoday.ir/ha/news/world-i18242-malaysia_ta_kori_jakadan_koriya_ta_arewa
Kasar Malaysia ta sanar da korar jakadan Koriya ta Arewa daga kasarta, a daidai lokacin da dangantaka ta yi tsami tsakanin kasashen biyu bayan kisan dan uwan shugaba Kim Jong-Un a filin jirgin saman Kuala Lampur.
(last modified 2018-08-22T06:59:46+00:00 )
Mar 05, 2017 07:48 UTC
  • Malaysia Ta Kori Jakadan Koriya Ta Arewa

Kasar Malaysia ta sanar da korar jakadan Koriya ta Arewa daga kasarta, a daidai lokacin da dangantaka ta yi tsami tsakanin kasashen biyu bayan kisan dan uwan shugaba Kim Jong-Un a filin jirgin saman Kuala Lampur.

Wata sanarwa daga ma'aikatar harkokin wajen ta Malaysia ta ce daga jiya Asabar jakadan na Koriya ta Arewa ba shi da wani matsayi a kasar.

Wannan dai na zuwa ne bayan da kasar ta Malaysia ta bukaci shugaba Kim Jong-Un ya nemi gafara a gare ta saboka kalamensa na cacakar hukumomin kasar akan binciken da suke kan kisan dan uwansa Kim Jong-Nam.

Ko baya ga wannan matakin Malaysia ta ce daga ranar 6 ga watan Maris ta dakatar da yarjejeniyar dake tsakanin kasashen biyu ta shige da fice ba tare da takardar visa ba.