Mutane 62 Suka Mutu A Gobara Daji a Portugal
Hukumomi a Portugal sun ce a kalla mutane 62 ne suka mutu a mummun gobara gandun daji data aukawa yankin Leiria a tsakiyar kasar.
Gobara wacce ta tashi jiya da rana a garin Pedrogao Grande, ta kuma yi sanadin jikkatar mutane sama da hamsin ciki har da jami'an kwana-kwana guda takwas a cewar sakataren gwamnatin na harkokin cikin gidan kasar Jorge Gomes.
Wannan dai ita ce gobara daji mafi muni da aka taba gani a shekarun baya bayan nan a wannan kasa a cewar fira ministan kasar Antonio Costa.
An dai zuba jami'an kashe gobara kimanin 900 da kuma motoci 300 domin kashe wutar wacce har tsakiyar wannan ranar tana ci a wasu bangare.
Tuni dai gwamnatin kasar ta ayyana zamen makoki na kwanaki uku tun daga yau Lahadi domin juyayin wandanda suka mutu a wanna iftila'in.