Harin Bindiga Yayi Sanadiyar Mutanwar Mutane Biyu A Jamus
https://parstoday.ir/ha/news/world-i22734-harin_bindiga_yayi_sanadiyar_mutanwar_mutane_biyu_a_jamus
Harin bindiga da aka kai wajen gidan wani rawa daren jiya assabar a kasar Jamus yayi sanadiyar mutuwar mutane biyu tare da jikkata wasu da dama na daban.
(last modified 2018-08-22T07:00:28+00:00 )
Jul 30, 2017 07:24 UTC
  • Harin Bindiga Yayi Sanadiyar Mutanwar Mutane Biyu A Jamus

Harin bindiga da aka kai wajen gidan wani rawa daren jiya assabar a kasar Jamus yayi sanadiyar mutuwar mutane biyu tare da jikkata wasu da dama na daban.

Kamfanin dillancin labaran Jamus ya nakalto jami'an 'yan sandar kasar na cewa a daren jiya Assabar wani  dan bindiga ya buda wuta a wani gidan rawa na garin Constance dake jihar Baden Wurttemberg, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane biyu tare da jikkata wasu da dama na daban.

Har yanzu ba a bayyana dalilin kai wannan hari ba.

Bisa rahoton jami'an 'yan sanda, wanda ake zarkin kai harin, matashi ne mai shekaru 34 a duniya, kuma bayan fitowar sa daga cikin gidan rawan jami'an 'yan sanda sun bindige shi, inda ya samu mumunan rauni sannan ya cika bayan an isa  asibiti.