Venezuela : Tattaunawa Tsakanin Gwamnati Da 'Yan Adawa Ta Yi Armashi
https://parstoday.ir/ha/news/world-i25973-venezuela_tattaunawa_tsakanin_gwamnati_da_'yan_adawa_ta_yi_armashi
Wakilan gwamnati da na 'yan adawa a Venezuela sun kamalla zagayen farko na tattaunawar da suke a Jamhuriyar Dominican domin samun mafita a rikicin siyasar da ya dabaibaye kasar.
(last modified 2019-04-27T09:55:10+00:00 )
Dec 03, 2017 02:22 UTC
  • Venezuela : Tattaunawa Tsakanin Gwamnati Da 'Yan Adawa Ta Yi Armashi

Wakilan gwamnati da na 'yan adawa a Venezuela sun kamalla zagayen farko na tattaunawar da suke a Jamhuriyar Dominican domin samun mafita a rikicin siyasar da ya dabaibaye kasar.

Duk da cewa bangarorin basu cimma matsaya ba, amma an samu ci gaba sosai a tattaunawar a cewar shugaba Danilo Medina na Jamhuriyar ta Dominican.

Kasancewar bangarorin basu kai ga cimma matsaya ba zasu sake haduwa a birnin Saint-Domingue a ranar 15 ga watan nan na Disamba da muke ciki, da zumar samun mafita a cewar sanarwar bai daya ta karshen tattaunawar.

Sanarwa kashen tattaunawar ta ce dukkan bangarorin biyu sun nuna da gaske su ke a yunkurin samun fahimtar juna kan mummunan rikicin siyasa dana tattalin arziki da ya ki ci yaki cinyewa a kasar ta Venezuela.