Kasafin Kudin Amurka Zai Kara Kawo Talauci A Kasar
Sanatan Jahar Vermont na Amurka ya bayyana cewa kasafin kudin gwamnatin Trump shi zai kara dagula al'amuran tattalin arziki, talauci da kuma tabarbarewa tarbiya a kasar
Shugaban kasar Amirka Donald Trump ya kaddamar da kashi biyu na kasafin kudin shekara ta 2019 tare da neman zuba makudan kudade a bangaren tsaro.
Shirin kasafin kudin na dala miliyan 4.4 wanda 'yan majalisar kasar ke yi wa kallo irin na neman shawara ya janyo suka daga bangaren masu ra'ayin rikau wadanda suke wa 'yan jam'iyyar Republican kallon masu almubazzarnci da kudi. tuni dai wasu suka bukaci 'yan majalisar ta Amirka da su yi watsi da kasafin kudin shugaban kasa.
Sanata Bernie Sanders ya ce shugaba Trump so yake kai tsaye ya rage harajin bilyoyin daloli ga manyan kamfanonin kasar taa hanyar yanke insharar tallakawan kasar.