Birtaniya: Ana Ci Gaba Da Mayar Wa Boris Johnson Martani
https://parstoday.ir/ha/news/world-i32674-birtaniya_ana_ci_gaba_da_mayar_wa_boris_johnson_martani
Shugaban Jam'iyyar Conservative na kasar Birtaniya Brandon Lewis ya kirayi tsohon ministan harkokin Wajen Birtaniyan Boris Johnson da ya nemi gafara akan cin zarafin da ya yi wa mata musulmi masu sanya nikabi
(last modified 2018-08-22T07:02:13+00:00 )
Aug 08, 2018 03:03 UTC
  • Birtaniya: Ana Ci Gaba Da Mayar Wa Boris Johnson Martani

Shugaban Jam'iyyar Conservative na kasar Birtaniya Brandon Lewis ya kirayi tsohon ministan harkokin Wajen Birtaniyan Boris Johnson da ya nemi gafara akan cin zarafin da ya yi wa mata musulmi masu sanya nikabi

Boris Johnson ya kwantanta  matan masu sanya kallabin da su ke rufe fuskarsu da shi, Burkaa da cewa;  sun yi kama da masu fashi da makami a cikin Banki.

Shi ma Alistair Burt da shi ne babban jami'i mai kula da harkokin Afirka da gabas ta tsakiya a ma'aikatar harkokin wajen Birtaniy, ya ce furucin na Johnson cin zarafi ne.

Ita ma Majalisar musulmin Birtaniya ta bukaci ganin tsohon ministan harkokin wajen na Birtaniya ya nemi gafara.

A cikin watannin bayan nan a nahiyar turai an tsananta muzanta suturar hijabi da matan musulmi suke sanyawa.