Amurka : Hillary Clinton Ta Soki Siyasar Trump
https://parstoday.ir/ha/news/world-i33567-amurka_hillary_clinton_ta_soki_siyasar_trump
Clinton wacce tashar talabijin din CNN ta yi hira da ita ta ce salon mulkin Trump ya raunana aiki da doka a cikin kasar
(last modified 2019-04-27T09:55:10+00:00 )
Oct 11, 2018 08:51 UTC
  • Amurka : Hillary Clinton Ta Soki Siyasar Trump

Clinton wacce tashar talabijin din CNN ta yi hira da ita ta ce salon mulkin Trump ya raunana aiki da doka a cikin kasar

Hillary Clinton ta kuma zargi shugaban na Amurka da ba da dama ga batun cin hanci da rashawa ya watsu a cikin kasar da kuma a tsakanin na kusa da shi da su ka hada da iyalansa.

Tsohuwar ministar harkokin wajen ta kasar Amurka ta ci gaba da cewa; Ahalin da ake ciki a yanzu, al'ummar kasar sun dawo daga rakiyar cibiyoyi da dama na kasar da su ka hada da coci-coci da kuma majalisar dokoki

Hillary Clinto ta zargi Trump da halayyar danniya  saboda yadda yake jinjinawa 'yan kama karya.

Saboda karatowar zabuka a Kasar ta Amurka, manyan jam'iyyun biyu na kasar sun bude sukar junansu da tuhumarsu da rashin siyasa mai inganci.