Nan Da 'Yan Kwanaki Amurka Zata Bayyana Wanda Ya Kashe Khashoggi
https://parstoday.ir/ha/news/world-i34139-nan_da_'yan_kwanaki_amurka_zata_bayyana_wanda_ya_kashe_khashoggi
Shugaba Donald Trump na Amurka ya bayyana cewa nan da 'yan kwanaki masu zuwa kasarsa zata yi bayyana kan wanda ya kashe dan jaridan nan Jamel Khashoggi.
(last modified 2018-11-18T10:08:54+00:00 )
Nov 18, 2018 10:08 UTC
  • Nan Da 'Yan Kwanaki Amurka Zata Bayyana Wanda Ya Kashe Khashoggi

Shugaba Donald Trump na Amurka ya bayyana cewa nan da 'yan kwanaki masu zuwa kasarsa zata yi bayyana kan wanda ya kashe dan jaridan nan Jamel Khashoggi.

Da yake sanar da hakan ga 'yan jarida, Trump ya ce nan da kwana biyu za'a fitar da cikaken rahoto kan wanda ya aikata kisan.

Wannan dai na zuwa ne bayan da hukumar leken asirin Amurka ta CIA, ta sanar cewa yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohamed Ben Salman ne ya bada umurnin kashe dan jaridan, koda yake Bin Salman din ya musanta hakan.

A ranar 2 ga watan Oktoba da ya gabata ne aka kashe dan jaridan mai sukan masarautar saudiyya a karamin ofishin jakadancin Saudiyyar na birnin Santambul a Turkiyya.