Shugaban Venezuela ya Yi Allawadai Da Shishigin Amurka A Lamuran Kasarsa
https://parstoday.ir/ha/news/world-i34760-shugaban_venezuela_ya_yi_allawadai_da_shishigin_amurka_a_lamuran_kasarsa
Shugaban kasar Venezuela Nicolas Madoro ya yi rantsuwara kama aiki a matsayin shugaban kasar Venezuela karo na biyu a jiya Alhamis.
(last modified 2019-08-10T14:54:46+00:00 )
Jan 11, 2019 06:41 UTC
  • Shugaban Venezuela ya Yi Allawadai Da Shishigin Amurka A Lamuran Kasarsa

Shugaban kasar Venezuela Nicolas Madoro ya yi rantsuwara kama aiki a matsayin shugaban kasar Venezuela karo na biyu a jiya Alhamis.

Majiyar muryar JMI daga Caravas ta bayyana cewa shugaba Madoro ya zargi kasashen Amurka da kuma kasashen kungiyar LIMA da yi masa zagon kasa, ya kuma bayyanasu a matsayin wadanda suke son dawo da mulkin kama karya a kasar Venezuela. 

A ranar 4 ga watan  Jenerun da muke ciki ne kungiyar LIMA ta kasashen yankin laten Amurka suka bukaci shugaba Madoros da ya sauka daga kan kujerar shugabancin kasar Venezuela don a sake zabe mai inganci a kasar, sannan sun sha alwashin cewa ba zasu taba amincewa da shi a matsayin halattaccen shugaban kasar Venezueala ba. 

Shugaba Nicolas Madoro dai ya zama shugaban kasar Venezuela ne a shekara ta 2013 bayan rasuwar shuaba Hogo Cheves. Sannan aka sake zabensa a karo na biyu a shekaran da ta gabata. 

Kasashenkungiyar Lima dai suna hada da Venezuelan, Agentina m Brazil, Canada, Chilli, Colombia , Costorica, Gwatamala, Hundurus, Panama, Paragua, Preu, Mixico da Sient KLusyo.