Gwamnatin Kasar China Na Ci Gaba Da Takura Musulmi
https://parstoday.ir/ha/news/world-i35318-gwamnatin_kasar_china_na_ci_gaba_da_takura_musulmi
Gwamnatin kasar china ta lakafa kamarori a yankin da muuslmi suke da zama domin sanya ido a kansu da kuma harkokinsu.
(last modified 2019-08-10T10:24:46+00:00 )
Feb 22, 2019 09:58 UTC
  • Gwamnatin Kasar China Na Ci Gaba Da Takura Musulmi

Gwamnatin kasar china ta lakafa kamarori a yankin da muuslmi suke da zama domin sanya ido a kansu da kuma harkokinsu.

shafin yada labarai na Magrib yaum ya bayar da rahoton cewa, a ci gaba da daukar matakan takurawa kan musulmi, gwamnatin kasar china ta lakafa kamarori a yankin Sing Kiyang na musulmi domin sanya ido a kansu da kuma dukkanin zirga-zirgarsu da sauran harkokinsu na yau da kullum.

Rahoton ya ce wadannan kamarori suna sanya ido a kn musulmi sama da miliyan biyu da rabi da ke yankin, wadanda suke fuskantar gallazawa daga jami’an tsaron gwamnatin kasar ta China.

Yanzu haka akwai miliyoyon muusulmi da China ta tsare a wani sansani tare da hana su gudanar da harkokinsu, inda ake tilasta su cin naman alade da kuma shan giya, kamar yadda a cikin watan azumi ake tilasta su cin abinci da rana.