An Bukaci Gudanar Da Zaben Raba Gardama Kan Makomar Sarautar Ingila
https://parstoday.ir/ha/news/world-i4210-an_bukaci_gudanar_da_zaben_raba_gardama_kan_makomar_sarautar_ingila
Jam'iyyar Republican ta kasar Britania ta bukaci a gudanar da zaman raba gardama
(last modified 2018-08-22T06:58:10+00:00 )
Apr 21, 2016 23:01 UTC
  • An Bukaci Gudanar Da Zaben Raba Gardama Kan Makomar Sarautar Ingila

Jam'iyyar Republican ta kasar Britania ta bukaci a gudanar da zaman raba gardama

Jam'iyyar Republican ta kasar Britania ta bukaci a gudanar da zaben raba gardama a kasar bayan mutuwar Saraunia Elizabath II. Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto sakatarin gudanarwa na jam'iyyar Graham Smith yana fadar haka a jiya Alhamis a dai dai lokacinda ake bukukuwan cika shekara 90 da haihuwar Sarauniyar a birnin London.

Smith ya kara da cewa mafi yawan mutanen kasar Britania basa da ra'ayin ci gaba da tsarin sarauta a kasar, don haka akwai bukatar a gudanar da zaben raba gardama kan makamar tsarin sarauta na kasar,  wanda babu abinda yake tunatarwa,  sai irin zaluncin da tsarin ya aiwatar a duniya.

A halin yanzu dai Saraunia Elizabeth ta ciki shekaru 63 kan kujerar sarautar kasar Britania, sannan ita ce sarauniyar wasu kasashe 16 a duniya masu cin gashin kansu. Banda haka Saraunair Ingila ce  shugabar kungiyar Commanwealth ta kasashe ranon ingila 54 a duniya.