Sudan: Kamun Babban Mai Fatauncin Mutane
An Kame Mai Fataucin 'Yan gudun hijira A Kasar Sudan
Jaridar al-Yaum Sabi'i, da ake bugawa a kasar Masar ta ambato wani jami'in kasar Sudan yana cewa; Mutumin da aka kama din dan asalin kasar Erittera ne mai suna Murid Mudhany.
Mutumin wanda ake bai wa sunan; 'Janar' ana zarginsa da mutuwar mutane 359 a cikin ruwan kasar Italia a 2013.
Rahoton ya ci gaba da cewa; Kungiyar da ta ke fada da aikata laifuka a Birtaniya da kuma cibiyar tattara bayanai da tsaro ta kasar Italiya, sun rika bin diggidin mutumin inda su ka yi nasarar gano mabuyarsa da suka sanar da gwamnatin Khartum.
Wasu tuhume-tuhumen da Mudhani ya ke fukanta sun hada da mummunar mu'amala da 'yan gudun hijira da jefa rayuwarsu cikin hatsari.