-
Ana Zaben Kananen Hukumomi A Ivory Coast
Oct 13, 2018 08:21Yau Asabar al'ummar Ivory Coast sama da miliyan shida da sukayi rejista ke kada kuri'a a zabukan wakilan kananan hukumomin kasar.
-
An Nada 'Yar Afrika Ta Farko A Matsayin Shugabar Kungiyar OIF
Oct 13, 2018 03:41An nada Louise Mushikiwabo 'yar kasar Ruwanda a matsayin shugaban kungiyar kasashe masu magana da harshen faransanci "Francophone" a takaice.
-
Zimbabwe : An Haramta Zanga-zanga Kan Karin Haraji
Oct 10, 2018 02:14Rundunar 'yan sanda a Zimbabwe, ta haramtawa kungiyoyin kwadago na kasar gudanar da zanga-zangar nuna adawa da karin haraji kan aikewa da kudade.
-
MDD Ta Bukaci Aljeriya Ta Daina Tiso Keyar Bakin Haure
Oct 10, 2018 02:13Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci Aljeriya data dakatar da korar bakin haure 'yan Afrika zuwa jamhuriyar Nijar.
-
Ministan Kudin Afrika Ta Kudu Ya Yi Murabus
Oct 10, 2018 02:12Ministan kudin Afrika ta Kudu, Nhlanhla Nene, ya yi murabus daga mukaminsa, bayan kwashe kwanaki na kiraye kirayen hakan daga 'yan adawa bisa zarge zargen rashawa.
-
Ana Zaman Makoki A D.R Congo
Oct 08, 2018 07:46A Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo, ana zaman makoki na kwanaki uku bayan mummunan hatsarin tankai mai da ya yi sanadin mutuwar mutum akalla 60.
-
Malamman Addini Na G5 Sahel Na Taro A Mauritania
Oct 04, 2018 15:22Jagororin malamai da sarakunnan gargajiya na kungiyar kasashen gungun G5 Sahel, na taro a birnin Nouakchot na kasar Mauritania, kan yaki da tsatsaran ra'ayin addini.
-
Bam Ya Kashe Sojojin Burkina Faso Akalla 6
Oct 04, 2018 12:16Wani bam da aka dasa kan hanya ya yi sanadiyyar mutuwar sojoji akalla shida, da kuma raunana wasu a gabashin Burkina Faso.
-
Nijar Ta Kori Likitar (Doctors Without Borders), Saboda Zuzuta Alkalumman Mace Macen Yara
Oct 03, 2018 14:25Hukumomi a Jamhuriya Nijar sun sanar da korar wata likitar yara ta kungiyar likitoci marar iyaka wato (Doctors Without Borders) ta Switzerland, saboda zarginta da azuzuta alkalumman mace-macen yara kanana a garin Magaria dake jihar Zinder.
-
Guinea Na Bikin Cika Shekara 60 Da Samun 'Yancin Kai
Oct 02, 2018 07:53Yau, Guinea, ke bikin cika shekaru 60 da samun 'yancin kai daga turawan mulkin mallaka na Faransa.