Ana Zaben Kananen Hukumomi A Ivory Coast
Oct 13, 2018 08:21 UTC
Yau Asabar al'ummar Ivory Coast sama da miliyan shida da sukayi rejista ke kada kuri'a a zabukan wakilan kananan hukumomin kasar.
Yan takara dubu ashirin da biyu ne ke takara a zaben, saidai jam’iyyar tsohon Shugaban kasar Laurent Gbagbo dake tsare a kotun ICC ta kaucewa zaben.
Ana dai ganin zaben zai kasance zakarin gwajin dafi wa hukumar zaben kasar a zaben Shugaban kasar na shekara ta 2020.
Tags