Malamman Addini Na G5 Sahel Na Taro A Mauritania
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i33484-malamman_addini_na_g5_sahel_na_taro_a_mauritania
Jagororin malamai da sarakunnan gargajiya na kungiyar kasashen gungun G5 Sahel, na taro a birnin Nouakchot na kasar Mauritania, kan yaki da tsatsaran ra'ayin addini.
(last modified 2018-10-04T15:22:53+00:00 )
Oct 04, 2018 15:22 UTC
  • Malamman Addini Na G5 Sahel Na Taro A Mauritania

Jagororin malamai da sarakunnan gargajiya na kungiyar kasashen gungun G5 Sahel, na taro a birnin Nouakchot na kasar Mauritania, kan yaki da tsatsaran ra'ayin addini.

taron dake samun tallafin kungiyar kasashen Turai, na zuwa ne a daidai lokacin da tsatsauran ra'ayin addinin islama ta hanyar wasu haramtatun kungiyoyi ke kara kamari a yankin na Sahel.

Mahalarta taron daga kasashen yankin zasu maida hankali wajen jan hankalin matasa akan kaurace wa kiraye kirayen ire wadannan kungiyoyin musamman Boko Haram dake zaman babbar barazana a yankin.

Kungiyar Boko Haram dai na amfani da matasa wajen yada muggan akidunta da kuma kai hare hare ta'addanci a kasashen Najeriya, Nijar Kamaru da Chadi.