-
Sojojin Nijar Da Chadi Sun Kashe 'Yan Boko Haram 123
Oct 01, 2016 07:07Rundunar sojin Nijar ta ce dakarunta da hadin gwiwar na Chadi sun hallaka 'yan ta'addan Boko Haram 123, a ci gaba da samamen da suke kaiwa a yankin Diffa dake kudu maso gabashin kasar.
-
Nijar : Bakuwar Cuta Ta Kashe Mutane 25
Sep 29, 2016 08:35Ma'aikatar lafiya a Jamhuriya Nijar ta sanar da cewa mutane 25 kawo yanzu suka rasa rayukansu sanadin kamuwa da bakuwar cutar nan ta zazzabi wace asalinta ta dabbobi ce amma takan iya kama mutane.
-
An tsawaita dokar ta bace a jihar Diffa dake kudu maso gabashin Nijer
Sep 29, 2016 02:15Gwamnatin Nijer ta sake tsawaita dokar ta bace a jihar Diffa dake kudu maso gabashin kasar.
-
Malaman Jami'an Nijar Sun Fara Wani Yajin Aiki Don Neman Hakkokinsu
Sep 19, 2016 06:55Malaman jami'oi a Jamhuriyar Nijar sun fara wani yajin aiki na mako guda don nuna rashin jin dadinsu da kin biyansu albashin da suke bin gwamnatin kasar.
-
Nijar : An Sako Makusantan Hama Amadou
Sep 18, 2016 23:25Babbar Jam'iyyar adawa ta MODEN Lumana a Jamhuriya Nijar ta tabbatar da sakin wadansu makusantan shugaban jam'iyyar su bakwai ciki har da Sumana Sanda wani tsohon ministan lafiya, bayan shafe wata 10 suna daure a gidan kaso.
-
Sojojin Nijar Da Chadi Sun Kashe 'Yan Boko Haram 38 A Difa
Sep 17, 2016 13:35Hukumomin a Jamhuriya Nijar sun sanar da cewa dakarun kasar hadin gwiwa dana Chadi sun hallaka 'yan ta'addan Boko Haram 38 a yankin Difa dake kudu maso gabashin kasar.
-
An Kashe Mayakan Boko Haran A Kudu Maso gabashin Niger
Sep 16, 2016 00:47An kashe mayakan kungiyar Boko Haram da dama a yankin Difa kudu maso gabcin Jumhuriyar Niger.
-
Tattaunawar Nijer da Libiya kan harakokin tsaro
Sep 09, 2016 05:58Magabatan Kasashen Nijer da Libiya sun tattauwa a kan harakokin tsaro
-
Nijar : Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane 38
Sep 09, 2016 00:31A jamhuriya Nijar wasu sabbin alkaluma da ofishin kula da harkokin jin kai na MDD ya fitar sun nuna cewa, ya zuwa yanzu akalla mutane 38 ne suka rasa rayukansu kana wasu sama da 92,000 suka rasa gidajensu sakamakon bala'in ambaliyar ruwa da ta shafi wasu sassan kasar a 'yan watannin da suka wuce.
-
Wani Gungun Mayaka Ya yi Barazanar Kaiwa Nijar Hari
Sep 07, 2016 12:04Wani gungun mayaka dake kiran kansa mai fafatukar kwatowa kabilar tsirarun tubawa hakkinsu, ya yi barazanar kaiwa Nijar hari.