An BUde Taron Farko Na Kusanci A Tsakanin Mazhabobin Musulunci A Masar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i10166-an_bude_taron_farko_na_kusanci_a_tsakanin_mazhabobin_musulunci_a_masar
Taron hadin kan mazahabobi a masar
(last modified 2018-08-22T06:58:49+00:00 )
Aug 26, 2016 07:16 UTC
  • An BUde Taron Farko Na Kusanci A Tsakanin Mazhabobin Musulunci A Masar

Taron hadin kan mazahabobi a masar

An budetaron farko na  hadin a tsakanin mazhabobin musulunci  a kasar Masar.

Wani Malamin Jami'ar Azhar wanda ya gabatar da jawabi a wurin taron, Ahmad Karimah yayi ishara da rawar da Azhr ta taka wajen hada kan mazhabobin musulunci da kusanto da fahimtar juna, sannan ya kara da cewa; Mazhabobin Shi'a da Sunna basu kafrita junansu, kuma jami'ar Azhar ta yarda da yawaitar mazhabobi.

Malamin ya ci gaba da cewa kawo ya zuwa yanzu malaman mazhabar shia a Iraki da Iran sun fitar da fatawowi 22 da haramta cin zarafin duk wani abu da ahlussunah su ke girmamawa.