Misrawa 16 sun rasu kafin fara aikin hajjin bana
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i10849-misrawa_16_sun_rasu_kafin_fara_aikin_hajjin_bana
Ministan Lafiya na Masar ya sanar da cewa ya zuwa yanzu Maniyata aiki hajji 'yan kasar 16 ne suka rasa rayukansu a Saudiya.
(last modified 2018-08-22T06:58:54+00:00 )
Sep 10, 2016 06:40 UTC
  • Misrawa 16 sun rasu kafin fara aikin hajjin bana

Ministan Lafiya na Masar ya sanar da cewa ya zuwa yanzu Maniyata aiki hajji 'yan kasar 16 ne suka rasa rayukansu a Saudiya.

Ministan ya bayyana hakan ne bayan wani hadarin Mota da ya yi sanadiyar rasuwar Bamisire guda a kasar ta Saudiya.inda ya ce sauren Misrawa 15 din sun rasa rayukansu ne a dalilin rashin lafiya.

A nasa bangare Ministan tsare-tsare na kasar ta Masar Ashraf Al-Arabie da ke jagorantar mahajjatan na Masar ya ce A shekarar Bana Maniya aiki hajji na Kasar Dubu 62 da 511 ne za su sauke farari.

Bisa wani rahoto da Jaridar Al-Akhbar ta kasar Labnon ta watsa, bayan Jumhoriyar musulinci ta Iran, Masar ce kasa ta biyu ta tayi asarar yawan mahajatanta a shekarar da ta gabata sanadiyar turmutsutsun Mina.