Nuna Tsananin Damuwa Kan Aiwatar Da Kisan Kiyashi A Kasar Burundi
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i11329-nuna_tsananin_damuwa_kan_aiwatar_da_kisan_kiyashi_a_kasar_burundi
Tawagar bincike ta Majalisar Dinkin Duniya dake kasar Burundi ta nuna damuwarta kan yiyuwar aiwatar da kisan kiyashi a kasar.
(last modified 2018-08-22T06:58:57+00:00 )
Sep 20, 2016 13:55 UTC
  • Nuna Tsananin Damuwa Kan Aiwatar Da Kisan Kiyashi A Kasar Burundi

Tawagar bincike ta Majalisar Dinkin Duniya dake kasar Burundi ta nuna damuwarta kan yiyuwar aiwatar da kisan kiyashi a kasar.

Tawagar bincike ta Majalisar Dinkin Duniya da ke gudanar da aiki a kasar Burndi ta sanar da cewa: Gwamnatin kasar ita ke da alhakin matsalolin ci gaba da take hakkokin bil-Adama da suke faruwa a kasar, kuma akwai yiyuwar cin zarafin bil-Adama a kasar zai kai ga matakin aiwatar da kisan kiyashi.

Tawagar ta kara da cewa: Gwamnatin Burundi da msu goya bata baya suna daga cikin masu take hakkokin bil-Adama a kasar.