Nijer : An Fara Sanar Da Kwarya-Kwarya Sakamakon Zabe
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i1156-nijer_an_fara_sanar_da_kwarya_kwarya_sakamakon_zabe
Hukumar zaben kasar wato CENI na sa ran fitar da sakamakon zaben ne cikin kwanaki uku.
(last modified 2018-08-22T06:57:51+00:00 )
Feb 23, 2016 05:06 UTC
  • Nijer : An Fara Sanar Da Kwarya-Kwarya Sakamakon Zabe

Hukumar zaben kasar wato CENI na sa ran fitar da sakamakon zaben ne cikin kwanaki uku.

Hukumar zabe mai zamen kan ta a jamhuriya Nijer ta fara sanar da kwarya-kwarya sakamakon zaben shugaban kasa gami dana 'yan majalisun dokoki da aka kada a ranakun Lahadi da Litinin din nan.

Sakamakon da aka fara fitarwa a cikin daren jiyya Litinin ya hada dana kasashen waje dana wasu yankunan kasar, inda a cikin kasar shugaban Mahamadu Issufu ne mai barin gado ke kan gaba da kaso 35,66%, sai dan takara na Moden Lumana Hama Amadu mai bi mishi da 31,54 %, yayin da Seyni Omar na MNSD Nasara keda 10,57% ; sai tsohon shugaba Mahamane Ousmane, 6,38 %.

A Najeriya dai Jami’an zaben na Nijar a Abuja, sun ayyana dan takarar MODEN LUMANA, Hama Amadou kan gaba, sai Muhamadou Issoufou na PNDS TARAYYA, sai kuma Seyni Oumarou na MNSD NASSARA, A jihohin Rivers da Edo dai Jam'iyyar PNDS - tarraya ce ta lashe zaben, yayin da a kasar kamaru 'yan hamaya suka ce sun rungumi kadara.

Hukumar zaben kasar dai ta Nijer wato CENI na sa ran fitar da sakamakon zaben ne cikin kwanaki uku.