Masar Ta Bukci Hadin Kai Tsakanin Kasashen Iran, Saudiyya, Masar da Indonesiya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i11605-masar_ta_bukci_hadin_kai_tsakanin_kasashen_iran_saudiyya_masar_da_indonesiya
Ministan harkokin wajen kasar Masar ya bukaci hadin kai tsakanin kasashen Iran, Masar, Saudiyya da Indonesiya da nufin farfado da ci gaban kasashe masu tasowa.
(last modified 2018-08-22T06:58:59+00:00 )
Sep 26, 2016 07:27 UTC
  • Masar Ta Bukci Hadin Kai Tsakanin Kasashen Iran, Saudiyya, Masar da Indonesiya

Ministan harkokin wajen kasar Masar ya bukaci hadin kai tsakanin kasashen Iran, Masar, Saudiyya da Indonesiya da nufin farfado da ci gaban kasashe masu tasowa.

A ganawarsa da jaridar Al-Yaumus-Sabi'i ta Masar: Ministan harkokin wajen kasar Samaha Shukri ya bayyana cewa: Samun hadin kai tsakanin kasashen Iran, Masar, Saudiyya da Indonesiya zai taimaka a fagen farfado da ci gaban kasashen masu tasowa.

Har ila yau Shukri ya jaddada matsayin kasarsa ta rashin amincewa da duk wani tsoma bakin kasashen waje a harkokin da suka shafi harkokin cikin gidan Masar.