Jamus za ta kafa sansanin Soja a Nijer
Kasar Jamus ta bayyana shirin ta na kafa Sansanin Soja a Jumhoriyar Nijer
Maku guda bayan da kasar Amurka ta sanar da kafa Sansanin Soja a Nijer, Jakadar Kasar Jamus a Nijer shima ya sanar da shirin kasar na kafa Sansanin Soja da zai taimakawa Dakarun dake yakar masu da'awar Jihadi a kasar Mali.
Jakadar ya kara da cewa Jamus a shirye take ta bayar da babbar gudumuwa a yankin sahara na kasashen Afirka, sannan ya bayyana Nijer din a matsayin babbar abokiya a fagen yaki da ta'addanci da kuma bakin haure.
A karshen watan Satumbar da ya gabata ne Gwamnatin kasar Amurka ta tabbatar da gina wani sabon Sansanin Soja da zai lakume miliyan 50 zuwa 100 na $ a jihar Agadez dake arewacin kasar ta Nijer.
kafin hakan dai, Kasar Amurka na da Sansanin Sojan sama a birnin Yamai fadar milkin kasar, inda daga can ne take taimakawa Sojojin MDD dake yaki da ta'addanci a kasar Mali kalkashin jagorancin kasar Faransa, da kuma Sojojin kasashen Murtaniya, Burkina Faso, Tchadi da ita kan ta Nijer din a fagen yaki da ta'addanci.
A wannan lahadi ne ake sa ran shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel za ta fara ziyarar aiki na kwanaki uku a kasashen Habasha , Nijer da Mali dan tattaunawa da shugabanni da kasashensu ke zama hanyoyi da bakin haure ke bi a kokarin su na zuwa kasashen Turai