Taron kai harin gare dangi a kan Kungiyar Boko haram
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i12442-taron_kai_harin_gare_dangi_a_kan_kungiyar_boko_haram
Manyan komondojin yankin tabkin Chadi sun fara gudanar da taro domin duba hanyoyin da ya kamata su bi wajen kai harin kare dangi kan kungiyar boko haram a Jumhoriyar Nijer
(last modified 2018-08-22T06:59:05+00:00 )
Oct 14, 2016 07:33 UTC
  • Taron kai harin gare dangi a kan Kungiyar Boko haram

Manyan komondojin yankin tabkin Chadi sun fara gudanar da taro domin duba hanyoyin da ya kamata su bi wajen kai harin kare dangi kan kungiyar boko haram a Jumhoriyar Nijer

Kamfanin dillancin labaran kasar Faransa ya habarta cewa A jiya Alkhamis Manyan komondojin kasashen Najeriya, Nijer , Chadi, Kamaru da kuma Benin sun fara gudanar da taro da nufin bincike kan hanyoyin kai hari kare danki kan kungiyar Boko haram a birnin Yamai na jumhoriyar Nijer.

A yayin buda taron, Ministan tsaron Nijer Hassoumi Massoudou ya bayyana cewa daga watan yunin da ya gabata zuwa yanzu kasashen Nijer, Chadi da Najeriya sun gudanar da aiyukan leken asiri da dama kan sansanonin kungiyar Boko haram kuma shakka babu wani aiki ya bada sakamako mai kyau wajen kai hari kan 'yan ta'addar.

Ministan ya kara da cewa hare-haren da Dakarun tsaron kasashen Chadi, Nijer da Najeriya ke kaiwa kan 'yan ta'addar na boko haram ya yi sanadiyar 'yanto yankuna da dama dake hanun 'yan boko haram din a baya.