Gwamnatin Niger Ta Jaddada Bykatar Yaki Da Yan Ta'adda A Kasar
Gwamnatin kasar Niger ta bayyana cewa yan ta'adda wadanda suke zaune a arewacin kasar Mali sune da alhakin tashe tashen hankula a arewacin kasar a cikin yan kwanakin da suka gabata.
Shafin yanar gizo na Africa Time ya nakalti ministan harkokin wajen kasar Niger Ibrahim Yakuba yana fadar haka a jiya Alhamis ya kuma kara da cewa kasar Niger bada da yan ta'adda a cikin kasar amma yan ta'adda daga arewacin kasar Mali sun addabi arewacin kasar suna kuma tada hankali a sauran kasashen da suke makobtaka da kasar ta Mali,
Yakuba ya kara da cewa a cikin kwanaki goma da suka gabata yan ta'adda daga arewacin kasar Mali sun kai hare hare har sau ukku a arewacin kasar ta Niger, sannan a gefe daya kuma a ranar talatan da ta gabata ne kungiyar Boko Haram suka shigo daga tarayyar Nigeria suka kai wani hare a yankin Difa na kudu maso gabacin kadar.
Daga karshe ministan ya jaddada anniyar gwamnatin kasar na ci gaba da fada da wadannan kungiyyo na yan ta'adda.