Karuwar Tauye Hakkin Bil'adama A kasar Sudan Ta Kudu
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i18530-karuwar_tauye_hakkin_bil'adama_a_kasar_sudan_ta_kudu
Majalisar Dinkin Duniya Ta yi Gargadi Akan Karuwar Tauye Hakkin Bil'adama A Kasar Sudan Ta Kudu Da Take Fama Da Yaki.
(last modified 2018-08-22T06:59:49+00:00 )
Mar 15, 2017 15:33 UTC
  • Karuwar Tauye Hakkin Bil'adama A kasar Sudan Ta Kudu

Majalisar Dinkin Duniya Ta yi Gargadi Akan Karuwar Tauye Hakkin Bil'adama A Kasar Sudan Ta Kudu Da Take Fama Da Yaki.

Shugabar hukumar kare hakkin bil'adama ta majalisar dinkin duniya, Yasmin Sooka, ta fada a yau laraba cewa; Abubuwa masu firgitarwa da tashin hankali suna faruwa, a kasar Sudan ta kudu,da su ka hada da yin fyade,kuma yin shirun kasashen duniya akai za iya kai wa ga kisan kiyashi.

Yasmin Sooka ta kara da cewa; Gwamnatin Sudan ta kudu da sojojinta, suna hulda da mutanen kasar ne a bisa kabilanci.

 A gefe daya, ministan sharia na kasar ta Sudan ta kudu John Luk Jok ya yi watsi da rehoton na majalisar dinkin duniya, yana mai cewa babu gaskiya a cikinsa.