Masar Ta yi Suka Ga Kasashen Da Su Ke Kare 'Yan ta'adda.
Pira ministan Masar Sharif Isma'ila ya ce; Harin ta'addanci na karshe da aka kai a kasar da akwai hannun wasu kasashen waje.
Pira ministan Masar Sharif Isma'ila ya ce; Harin ta'addanci na karshe da aka kai a kasar da akwai hannun wasu kasashen waje.
pira ministan kasar ta Masar, ya fadi haka ne a lokacin da ya ke gabatar da jawabi a gabana majalisar dokokin kasar.
Shi ma shugaban majalisar dokokin ta Masar Ali Abdul aal ya ce; gwmanatin kasar tana da tabbacin cewa harin da aka kai wa majami'u biyu a kasar, 'yan ta'addar sun yi amfani ne da na'urorin sadarwa na zamani haka nan abubuwa masu fashewa da shakka babu wasu kasashe ne su ka bayar da su.
A jiya talata ne dai majalisar dokokin kasar ta amince da dokar ta baci da aka kafa ta tsawon kwanaki uku a kasar.
A wasu hare-haren ta'addanci da aka kai wa majami'u biyu a Alexandria da kuma TAnta, an kashe mutane fiye da 40 yayinda wasu fiye da 100 su ka jikkata.