Amurka Ta Gargadi 'Yan Kasarta A Masar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i21066-amurka_ta_gargadi_'yan_kasarta_a_masar
Ofishin Jakadancin Kasar Amurka A Masar Ya Gargadi 'Yan Kasar sa Dangane Da Hare-Haren Ta'addanci
(last modified 2019-08-10T10:24:46+00:00 )
Jun 06, 2017 07:15 UTC
  • Amurka Ta Gargadi 'Yan Kasarta A Masar

Ofishin Jakadancin Kasar Amurka A Masar Ya Gargadi 'Yan Kasar sa Dangane Da Hare-Haren Ta'addanci

A cikin wata Sanarwa da ya fitar a wannan Talata, Ofishin Jakadancin kasar Amurka dake birnin Alkahira ya bukaci 'yan kasar dake son yin bulaguro zuwa kasar ta Masar da kuma wadanda suke zaune a kasar su dauki matakin taka tsatsan wajen guraren da suke shiga domin kaucewa hare-haren 'yan ta'adda.

Har ila yau Ofishin ya tabbatar da cewa duk wata ganawa da ma'aikatan Diplomasiyar kasar ke yi a wuraren addini a wajen birnin Alkahira, an dakatar da shi har zuwa wani lokaci.

A kwanakin baya dai an kai hare-haren ta'addanci a majami'ar mabiyar Addinin Kirista a kasar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwa da kuma jikkatar mutane da dama.