Faransa Za Ta Bada Kudin Kafa Sabuwar Rundunar Kasashen Yankin Sahel
Jul 04, 2017 02:16 UTC
Kasashen da su ka yankin Sahen sun kuduri kafa wata sabuwar rundunar hadin gwiwa domin fada da ta'addanci.
Kasashen da su ka yankin Sahen sun kuduri kafa wata sabuwar rundunar hadin gwiwa domin fada da ta'addanci.
Shugaban kasar Faransa Emanuel Macron wanda ya ziyarci kasar Mali a shekaran jiya, ya yi alkawalin bada kudin da su ka kai euro miliyan 8 da motocin soja 70 ga kasashe biyar na yankin Sahel domin kafa sabuwar rundunar.
Kasashen da za su kafa wannan rundunar sun kunshi Mali, Burkina Faso, Murtaniya, Nijar da Chadi.
Yankin na Sahel yana fuskantar matsalolin tsaro daga kungiyoyin Bokoharam, kuma 'masu tsaurin ra'ayin addini a kasar Mali.
Tags