Sojojin Nijer Sun Kashe Manoma 14
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i21984-sojojin_nijer_sun_kashe_manoma_14
Dakarun gwamnatin Jamhuriyar Nijar sun kashe wasu fararen hula a wani farmakin da suka ce na kuskure a yankin Abadam na jihar Diffa da ke kan iyakar kasar da Najeriya.
(last modified 2019-03-18T05:42:56+00:00 )
Jul 07, 2017 11:16 UTC
  • Sojojin Nijer Sun Kashe Manoma 14

Dakarun gwamnatin Jamhuriyar Nijar sun kashe wasu fararen hula a wani farmakin da suka ce na kuskure a yankin Abadam na jihar Diffa da ke kan iyakar kasar da Najeriya.

Rahotanni dake fitowa daga jumhoriyar niger na cewa Sojojin kasar sun kashe wasu fararen hula 14 a wani farmakin kuskure  da suke zaton  mayakan Boko Haram ne, a yankin Abadam  da ke kan iyakar kasar da Najeriya.

Wani babban jami'i a yankin, ya ce sojojin gwamnatin Nijar din na sintiri ne a wuraren da aka haramtawa mutane gittawa a yankin na Abadam cikin yankin Diffa, inda suka buda wuta kan talakwan, da aka gano cewa wasu manoma ne.

Biyu daga cikin wadanda sojin suka kashe  'yan kasar Nijar ne, sauran 12 kuwa bayanan mahukunta sun ce 'yan Najeriya ne. Lamarin dai na faruwa ne kwanaki uku da mayakan Boko Haram suka kashe mutane tara tare da yin awan gaba da wasu masu yawa.