Ambaliyar Ruwa Ta Lashe Rayukan Akalla Mutane 50 A Kasar Nijer
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i24061-ambaliyar_ruwa_ta_lashe_rayukan_akalla_mutane_50_a_kasar_nijer
Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da cewa: Bullar matsalar ambaliyar ruwa sakamakon saukar ruwan sama kamar da bakin kwarya a tsawon watanni uku ta lashe rayukan mutane akalla 50 a Jamhuriyar Nijer.
(last modified 2019-04-27T14:25:10+00:00 )
Sep 15, 2017 11:46 UTC
  • Ambaliyar Ruwa Ta Lashe Rayukan Akalla Mutane 50 A Kasar Nijer

Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da cewa: Bullar matsalar ambaliyar ruwa sakamakon saukar ruwan sama kamar da bakin kwarya a tsawon watanni uku ta lashe rayukan mutane akalla 50 a Jamhuriyar Nijer.

Ofishin Hukumar kula da ayyukan jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya "OCHA" a birnin Yamai fadar mulkin Jamhuriyar Niger ya fitar da rahoton cewa: A tsawon watanni uku da suka gabata an samu bullar ambaliyar ruwa sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a wasu jihohin kasar Niger da ta janyo hasarar rayukan mutane akalla 50 tare da raba wasu kimanin 120,000 da muhallinsu.

Ambaliyar ruwar ta fi yin barna ce a babban birnin kasar Yamai sannan garuruwan Dosso, Tillaberi, Maradi da Zinder.