Cutar Kwalara Ta Bulla A Yankin Yammacin Kasar Burundi
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i25121-cutar_kwalara_ta_bulla_a_yankin_yammacin_kasar_burundi
Mahukuntan Burundi sun sanar da bullar cutar kwalara a yankin da ke yammacin kasar, inda cutar ta fara lashe rayukan mutane.
(last modified 2018-08-22T07:00:53+00:00 )
Oct 22, 2017 14:49 UTC
  • Cutar Kwalara Ta Bulla A Yankin Yammacin Kasar Burundi

Mahukuntan Burundi sun sanar da bullar cutar kwalara a yankin da ke yammacin kasar, inda cutar ta fara lashe rayukan mutane.

Gwamnatin jihar Bubanza da ke yammacin kasar Burundi Tarsis New-Ngabu ya sanar da cewa: Tun bayan bullar cutar ta kwalara a jihar a tsawon makonni biyu da suka gabata ta lashe rayukan mutane akalla hudu, yayin da wasu kimanin 30 na daban suka kamu da cutar.

Jami'an kiwon lafiya a yankin jihar ta Bubanza sun bayyana cewa: Matsalar rashin tsabtaceccen ruwan sha ce ta janyo bullar cutar ta kwalara tare da jaddada bukatar aikewa da tallafin gaggawa da nufin ceto ran jama'a.

Kididdiga ta bayyana cewa: Mutane kimanin 3,140 ne suka kamu da cutar kwalara a watan Yuli zuwa Ogustan wannan shekara a lardunan kasar Burundi biyu, inda 117 suka rasa rayukansu kafin mahukuntan kasar suka samu nasarar shawo kan matsalar cutar.