Masar Ta Gindaya Sharadi Kafin Ta Inganta Alakarta Da Turkiya
Ma'aikatar harakokin wajen Masar ta ce sharadin inganta alaka da Turkiya shi ne hukumomin Ankara su daina yin katsa landan a al'amuran cikin gidan Masar.
Kamfanin dillancin labaran Irna ya nakalto Sameh Shoukry ministan harkokin wajen Masar na cewa babu wani canji da aka samu a alakar diplomasiya tsakanin kasashen Masar da Turkiya duk kuwa da cewa Alkahira nada ra'ayin lokaci ya yi da za a rage sabanin dake akwai tsakanin kasashen biyu.
Sameh Shoukry ya kara da cewa wajibi ne kasar Turkiya ta kawo karshen katsa landan din da take yi a al'amuran cikin gidan Masar kafin a dawo da alakar dake tsakanin kasashen biyu kamar yadda take a baya.
Alaka ta yi tsami ne tsakanin kasashen Turkiya da Masar tun bayan juyin mulkin da aka yi wa Shugaba Mursi a shekarar 2013, bayan da hukumomin Turkiya suka yi kakkausar suka a kan juyin mulkin.