Masar: Sojoji Sun Halaka 'Yan Tawaye 36 A Yankin Sinaa
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i29219-masar_sojoji_sun_halaka_'yan_tawaye_36_a_yankin_sinaa
Kakakin sojan kasar Masar Tamir al-Rufa'i ya fada a yau litinin cewa an kashe 'yan ta'addar ne a wani farmaki da aka kai musu a yankunan arewa da tsakiyar Sinaa.
(last modified 2018-08-22T07:01:35+00:00 )
Mar 19, 2018 08:46 UTC
  • Masar: Sojoji Sun Halaka 'Yan Tawaye 36 A Yankin Sinaa

Kakakin sojan kasar Masar Tamir al-Rufa'i ya fada a yau litinin cewa an kashe 'yan ta'addar ne a wani farmaki da aka kai musu a yankunan arewa da tsakiyar Sinaa.

Tamir Rufa'i ya ci gaba da cewa: A cikin kwanaki biyar da bayan nan, sojoji da 'yan sandan Masar sun yi nasarar gano makamai masu yawa da 'yan ta'addar suke amfani da su wajen kai hare-hare.

Bugu da kari, kakakin sojan na Masar ya sanar da kame wasu 'yan ta'addar su 345, haka nan lalata motar da aka makare da bama-bamai.

A ranar 9 ga watan Febrairu ne dai sojojin Masar tare da 'yan sanda su ka shelanta wani farmaki da suka bai wa suna: Sina 2018." da zummar kawar da 'yan ta'adda daga yankin.

Yankin Sina yana a matsayin wata tunga ce ta kungiyoyin 'yan ta'adda.