Nijer:'Yan Boko Haran Sun Kashe Mutane 7 A Jahar Diffa
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i29334-nijer_'yan_boko_haran_sun_kashe_mutane_7_a_jahar_diffa
Wasu 'yan bindiga da ake kyautata zaton' yan Boko Haram ne sun kai wani hari a kauyen Tumur dake jihar Diffa a cikin daren jiya wayewar wannan safiyar Juma’a inda suka kashe mutum bakwai tare da jikattaa wasu da dama na daban.
(last modified 2018-08-22T11:31:36+00:00 )
Mar 23, 2018 17:39 UTC
  • Nijer:'Yan Boko Haran Sun Kashe Mutane 7 A Jahar Diffa

Wasu 'yan bindiga da ake kyautata zaton' yan Boko Haram ne sun kai wani hari a kauyen Tumur dake jihar Diffa a cikin daren jiya wayewar wannan safiyar Juma’a inda suka kashe mutum bakwai tare da jikattaa wasu da dama na daban.

Rahotanni dake fitowa  daga daga yankin Diffa na  jamhuriya Nijar na  cewa 'yan boko haram sun sake kai wani mumunan hari a garin Tumur a daren jiya wayewar safiyar wannan juma'a, inda suka kashe mutane kimanin bakwai.

Harin dai na yammacin jiya Juma'a a cewar rahotanni ya tilastawa sojojin kasar janyewa daga yankin sa'o'i kadan bayan da maharan suka farbawa garin.mazauna yankin sun shaida cewa 'yan boko haram din sun kuma kwashe kayayaki da dama kafin su bar wajen.

Wasu Rahotanni na daban sun ce mutum biyar ne aka kashe.

Yankin Diffa dake iyaka da Najeriya na fama da matsalar harin kungiyar Boko haram, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar jami'an tsaro  da fararen hular kasar da dama da raba wasu na daban da mahalinsu, kamar yadda yankunan  Tahoua da Tilabery ke fama da hare-haren 'yan tawaye da masu da'awar jihadi dake fitowa daga kasashen Mali da Burkina faso.

Kawo yanzu babu wani karin bayyani da ya fito  daga  bangaren hukumomin yankin da ma na kasar baki daya.