Masar : Al'Sisi Ya Lashe Zabe Da Gagarimin Rinjaye
Kafofin yada labarai na gwamnati a Masar, sun ce shugaba, Abdel Fattah Al-Sissi, ya lashe zaben shugaban kasar da aka kammala kada kuri'arsa a jiya Laraba da sama da kasha 90%.
Bayanan sun kuma ce abokin hamayyarsa daya tilo, Musa Mostafa Musa, ya samu kashi 3% na yawan kuri'un da aka kada.
Dama kafin hakan da yammacin jiya, dan takaran Musa Mostafa, ya bayyana a cikin wata hira da wani gidan talabijin mai zaman kansa a Masar din cewa, ya amunce shan kaye a zaben, duba da kwarya kwarya sakamakon zaben da aka fara fitarwa.
Rahotanni daga kasar sun ce ba'a samu fitowar jama'a sosai ba a zaben da aka kwashe kwanaki uku ana kada kuri'arsa, duk da kiran da mahukuntan kasar suka yi da barazana cin tarar jama'ar da suka kaurace wa zaben.
Nasara Al'sisi a zaben bata zo da mamaki ba, kasancewar duk mutanen da ake ganin zasu yi tasiri a zaben an haramta masu tsayawa takara.